Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

95 At-Tīn ٱلتِّين

< Previous   8 Āyah   The Fig      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

95:1 وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيْتُونِ
95:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Inã rantsuwa da Attinu da Azzaitũn.

95:2 وَطُورِ سِينِينَ
95:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da Dũr Sĩnĩna.

95:3 وَهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ ٱلْأَمِينِ
95:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wannan gari amintacce.

95:4 لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَـٰنَ فِىٓ أَحْسَنِ تَقْوِيمٍ
95:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa.

95:5 ثُمَّ رَدَدْنَـٰهُ أَسْفَلَ سَـٰفِلِينَ
95:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, Muka mayar da shi mafi ƙasƙantar masu rauni

95:6 إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ فَلَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍ
95:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, saboda haka suna da sakamako wanda bã ya yankewa.

95:7 فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعْدُ بِٱلدِّينِ
95:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, bãyan haka mẽ ya sanya ka ka ƙaryata sakamako (wanda za a yi a bãyan Tãshin ¡iyãma)?

95:8 أَلَيْسَ ٱللَّهُ بِأَحْكَمِ ٱلْحَـٰكِمِينَ
95:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe Allah bã Shi ne Mafi mãsu hukunci kyãwon hukunci ba?