Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

85 Al-Burūj ٱلْبُرُوج

< Previous   22 Āyah   The Mansions of the Stars      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

85:1 وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلْبُرُوجِ
85:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Inã rantsuwa da sama mai taurãrin lissafin shekara.

85:2 وَٱلْيَوْمِ ٱلْمَوْعُودِ
85:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da yinin da aka yi alkawarin zuwansa,

85:3 وَشَاهِدٍ وَمَشْهُودٍ
85:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da yini mai shaidu, da yini da ake halarta a cikinsa

85:4 قُتِلَ أَصْحَـٰبُ ٱلْأُخْدُودِ
85:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
An la'ani mutãnen rãmi.

85:5 ٱلنَّارِ ذَاتِ ٱلْوَقُودِ
85:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wato wuta wadda aka hura.

85:6 إِذْ هُمْ عَلَيْهَا قُعُودٌ
85:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da suke a kan (gefen) ta a zazzaune.

85:7 وَهُمْ عَلَىٰ مَا يَفْعَلُونَ بِٱلْمُؤْمِنِينَ شُهُودٌ
85:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Alhãli sũ, bisa ga abin da suke aikatãwa ga mũminai, sunã halarce.

85:8 وَمَا نَقَمُوا۟ مِنْهُمْ إِلَّآ أَن يُؤْمِنُوا۟ بِٱللَّهِ ٱلْعَزِيزِ ٱلْحَمِيدِ
85:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ba su tuhumce su ba, fãce kawai domin sun yi ĩmãni da Allah Mabuwãyi, wanda ake gõdewa.

85:9 ٱلَّذِى لَهُۥ مُلْكُ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَىْءٍ شَهِيدٌ
85:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda Yake shi ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma Allah a kan kõme halarce Yake.

85:10 إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُوا۟ ٱلْمُؤْمِنِينَ وَٱلْمُؤْمِنَـٰتِ ثُمَّ لَمْ يَتُوبُوا۟ فَلَهُمْ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمْ عَذَابُ ٱلْحَرِيقِ
85:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne waɗanda suka fitini mũminai maza da mũminai mãta, sa'an nan ba su tũba ba to, sunã da azãbar Jahannama, kuma sunã da azãbar gõbara.

85:11 إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ لَهُمْ جَنَّـٰتٌ تَجْرِى مِن تَحْتِهَا ٱلْأَنْهَـٰرُ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْفَوْزُ ٱلْكَبِيرُ
85:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da gidãjen Aljanna, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashin gidãjen. Wancan abu fa shi ne rabo babba.

85:12 إِنَّ بَطْشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ
85:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne damƙar Ubangijinka mai tsanani ce ƙwarai.

85:13 إِنَّهُۥ هُوَ يُبْدِئُ وَيُعِيدُ
85:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne Shĩ, Shi ne Mai ƙãga halitta, kuma Ya mayar da ita (bãyan mutuwa).

85:14 وَهُوَ ٱلْغَفُورُ ٱلْوَدُودُ
85:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Shi ne Mai gãfara, Mai bayyana sõyayya.

85:15 ذُو ٱلْعَرْشِ ٱلْمَجِيدُ
85:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai Al'arshi mai girma

85:16 فَعَّالٌ لِّمَا يُرِيدُ
85:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai aikatãwa ga abin da Yake nufi.

85:17 هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلْجُنُودِ
85:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ko lãbãrin rundanõni yã zo maka.

85:18 فِرْعَوْنَ وَثَمُودَ
85:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fir'auna da samũdãwa?

85:19 بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ فِى تَكْذِيبٍ
85:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ã'aha! waɗanda suka kãfirta sunã cikin ƙaryatãwa.

85:20 وَٱللَّهُ مِن وَرَآئِهِم مُّحِيطٌۢ
85:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Alhãli, Allah daga bãyansu, Mai kẽwaye su ne (da saninSa).

85:21 بَلْ هُوَ قُرْءَانٌ مَّجِيدٌ
85:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ã'aha! Shi Alƙur'ãni ne mai girma.

85:22 فِى لَوْحٍ مَّحْفُوظٍۭ
85:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikin Allo tsararre.