Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
85:1
وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلْبُرُوجِ
85:1
Inã rantsuwa da sama mai taurãrin lissafin shekara. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:2
وَٱلْيَوْمِ ٱلْمَوْعُودِ
85:2
Da yinin da aka yi alkawarin zuwansa, - Abubakar Gumi (Hausa)
85:3
وَشَاهِدٍ وَمَشْهُودٍ
85:3
Da yini mai shaidu, da yini da ake halarta a cikinsa - Abubakar Gumi (Hausa)
85:4
قُتِلَ أَصْحَـٰبُ ٱلْأُخْدُودِ
85:4
An la'ani mutãnen rãmi. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:5
ٱلنَّارِ ذَاتِ ٱلْوَقُودِ
85:5
Wato wuta wadda aka hura. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:6
إِذْ هُمْ عَلَيْهَا قُعُودٌ
85:6
A lõkacin da suke a kan (gefen) ta a zazzaune. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:7
وَهُمْ عَلَىٰ مَا يَفْعَلُونَ بِٱلْمُؤْمِنِينَ شُهُودٌ
85:7
Alhãli sũ, bisa ga abin da suke aikatãwa ga mũminai, sunã halarce. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:8
وَمَا نَقَمُوا۟ مِنْهُمْ إِلَّآ أَن يُؤْمِنُوا۟ بِٱللَّهِ ٱلْعَزِيزِ ٱلْحَمِيدِ
85:8
Kuma ba su tuhumce su ba, fãce kawai domin sun yi ĩmãni da Allah Mabuwãyi, wanda ake gõdewa. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:9
ٱلَّذِى لَهُۥ مُلْكُ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَىْءٍ شَهِيدٌ
85:9
Wanda Yake shi ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma Allah a kan kõme halarce Yake. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:10
إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُوا۟ ٱلْمُؤْمِنِينَ وَٱلْمُؤْمِنَـٰتِ ثُمَّ لَمْ يَتُوبُوا۟ فَلَهُمْ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمْ عَذَابُ ٱلْحَرِيقِ
85:10
Lalle ne waɗanda suka fitini mũminai maza da mũminai mãta, sa'an nan ba su tũba ba to, sunã da azãbar Jahannama, kuma sunã da azãbar gõbara. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:11
إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ لَهُمْ جَنَّـٰتٌ تَجْرِى مِن تَحْتِهَا ٱلْأَنْهَـٰرُ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْفَوْزُ ٱلْكَبِيرُ
85:11
Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da gidãjen Aljanna, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashin gidãjen. Wancan abu fa shi ne rabo babba. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:12
إِنَّ بَطْشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ
85:12
Lalle ne damƙar Ubangijinka mai tsanani ce ƙwarai. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:13
إِنَّهُۥ هُوَ يُبْدِئُ وَيُعِيدُ
85:13
Lalle ne Shĩ, Shi ne Mai ƙãga halitta, kuma Ya mayar da ita (bãyan mutuwa). - Abubakar Gumi (Hausa)
85:14
وَهُوَ ٱلْغَفُورُ ٱلْوَدُودُ
85:14
Kuma Shi ne Mai gãfara, Mai bayyana sõyayya. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:15
ذُو ٱلْعَرْشِ ٱلْمَجِيدُ
85:15
Mai Al'arshi mai girma - Abubakar Gumi (Hausa)
85:16
فَعَّالٌ لِّمَا يُرِيدُ
85:16
Mai aikatãwa ga abin da Yake nufi. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:17
هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلْجُنُودِ
85:17
Ko lãbãrin rundanõni yã zo maka. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:18
فِرْعَوْنَ وَثَمُودَ
85:18
Fir'auna da samũdãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
85:19
بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ فِى تَكْذِيبٍ
85:19
Ã'aha! waɗanda suka kãfirta sunã cikin ƙaryatãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:20
وَٱللَّهُ مِن وَرَآئِهِم مُّحِيطٌۢ
85:20
Alhãli, Allah daga bãyansu, Mai kẽwaye su ne (da saninSa). - Abubakar Gumi (Hausa)
85:21
بَلْ هُوَ قُرْءَانٌ مَّجِيدٌ
85:21
Ã'aha! Shi Alƙur'ãni ne mai girma. - Abubakar Gumi (Hausa)
85:22
فِى لَوْحٍ مَّحْفُوظٍۭ
85:22
A cikin Allo tsararre. - Abubakar Gumi (Hausa)