Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

92 Al-Layl ٱللَّيْل

< Previous   21 Āyah   The Night      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

92:1 وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ
92:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.

92:2 وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ
92:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.

92:3 وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰٓ
92:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da abin da ya halitta namiji da mace.

92:4 إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ
92:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.

92:5 فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَٱتَّقَىٰ
92:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.

92:6 وَصَدَّقَ بِٱلْحُسْنَىٰ
92:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.

92:7 فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْيُسْرَىٰ
92:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.

92:8 وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسْتَغْنَىٰ
92:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.

92:9 وَكَذَّبَ بِٱلْحُسْنَىٰ
92:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.

92:10 فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْعُسْرَىٰ
92:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.

92:11 وَمَا يُغْنِى عَنْهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ
92:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).

92:12 إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ
92:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.

92:13 وَإِنَّ لَنَا لَلْـَٔاخِرَةَ وَٱلْأُولَىٰ
92:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.

92:14 فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًا تَلَظَّىٰ
92:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.

92:15 لَا يَصْلَىٰهَآ إِلَّا ٱلْأَشْقَى
92:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.

92:16 ٱلَّذِى كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
92:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.

92:17 وَسَيُجَنَّبُهَا ٱلْأَتْقَى
92:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.

92:18 ٱلَّذِى يُؤْتِى مَالَهُۥ يَتَزَكَّىٰ
92:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.

92:19 وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُۥ مِن نِّعْمَةٍ تُجْزَىٰٓ
92:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.

92:20 إِلَّا ٱبْتِغَآءَ وَجْهِ رَبِّهِ ٱلْأَعْلَىٰ
92:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.

92:21 وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ
92:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).