Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

37 Aş-Şāffāt ٱلصَّافَّات

< Previous   182 Āyah   Those who set the Ranks      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

37:1 وَٱلصَّـٰٓفَّـٰتِ صَفًّا
37:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).

37:2 فَٱلزَّٰجِرَٰتِ زَجْرًا
37:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.

37:3 فَٱلتَّـٰلِيَـٰتِ ذِكْرًا
37:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.

37:4 إِنَّ إِلَـٰهَكُمْ لَوَٰحِدٌ
37:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.

37:5 رَّبُّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ ٱلْمَشَـٰرِقِ
37:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.

37:6 إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنْيَا بِزِينَةٍ ٱلْكَوَاكِبِ
37:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.

37:7 وَحِفْظًا مِّن كُلِّ شَيْطَـٰنٍ مَّارِدٍ
37:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.

37:8 لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلْمَلَإِ ٱلْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍ
37:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.

37:9 دُحُورًا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌ وَاصِبٌ
37:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.

37:10 إِلَّا مَنْ خَطِفَ ٱلْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُۥ شِهَابٌ ثَاقِبٌ
37:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.

37:11 فَٱسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَآ ۚ إِنَّا خَلَقْنَـٰهُم مِّن طِينٍ لَّازِبٍۭ
37:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.

37:12 بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ
37:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.

37:13 وَإِذَا ذُكِّرُوا۟ لَا يَذْكُرُونَ
37:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.

37:14 وَإِذَا رَأَوْا۟ ءَايَةً يَسْتَسْخِرُونَ
37:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.

37:15 وَقَالُوٓا۟ إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا سِحْرٌ مُّبِينٌ
37:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."

37:16 أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَـٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ
37:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?

37:17 أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ
37:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"

37:18 قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَٰخِرُونَ
37:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."

37:19 فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌ وَٰحِدَةٌ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ
37:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.

37:20 وَقَالُوا۟ يَـٰوَيْلَنَا هَـٰذَا يَوْمُ ٱلدِّينِ
37:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."

37:21 هَـٰذَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ
37:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.

37:22 ۞ ٱحْشُرُوا۟ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ وَأَزْوَٰجَهُمْ وَمَا كَانُوا۟ يَعْبُدُونَ
37:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.

37:23 مِن دُونِ ٱللَّهِ فَٱهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلْجَحِيمِ
37:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.

37:24 وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْـُٔولُونَ
37:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.

37:25 مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ
37:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?

37:26 بَلْ هُمُ ٱلْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ
37:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.

37:27 وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَآءَلُونَ
37:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.

37:28 قَالُوٓا۟ إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ ٱلْيَمِينِ
37:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."

37:29 قَالُوا۟ بَل لَّمْ تَكُونُوا۟ مُؤْمِنِينَ
37:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.

37:30 وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَـٰنٍۭ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًا طَـٰغِينَ
37:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."

37:31 فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَآ ۖ إِنَّا لَذَآئِقُونَ
37:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."

37:32 فَأَغْوَيْنَـٰكُمْ إِنَّا كُنَّا غَـٰوِينَ
37:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."

37:33 فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍ فِى ٱلْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ
37:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.

37:34 إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِٱلْمُجْرِمِينَ
37:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.

37:35 إِنَّهُمْ كَانُوٓا۟ إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَآ إِلَـٰهَ إِلَّا ٱللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ
37:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.

37:36 وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوٓا۟ ءَالِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَّجْنُونٍۭ
37:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?

37:37 بَلْ جَآءَ بِٱلْحَقِّ وَصَدَّقَ ٱلْمُرْسَلِينَ
37:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.

37:38 إِنَّكُمْ لَذَآئِقُوا۟ ٱلْعَذَابِ ٱلْأَلِيمِ
37:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.

37:39 وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ
37:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.

37:40 إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ
37:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

37:41 أُو۟لَـٰٓئِكَ لَهُمْ رِزْقٌ مَّعْلُومٌ
37:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
Waɗannan sunã da abinci sananne.

37:42 فَوَٰكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ
37:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.

37:43 فِى جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ
37:43
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.

37:44 عَلَىٰ سُرُرٍ مُّتَقَـٰبِلِينَ
37:44
Abubakar Gumi (Hausa) :
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.

37:45 يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍۭ
37:45
Abubakar Gumi (Hausa) :
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.

37:46 بَيْضَآءَ لَذَّةٍ لِّلشَّـٰرِبِينَ
37:46
Abubakar Gumi (Hausa) :
Farã mai dãɗi ga mashãyan.

37:47 لَا فِيهَا غَوْلٌ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ
37:47
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,

37:48 وَعِندَهُمْ قَـٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ عِينٌ
37:48
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.

37:49 كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌ مَّكْنُونٌ
37:49
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.

37:50 فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَآءَلُونَ
37:50
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.

37:51 قَالَ قَآئِلٌ مِّنْهُمْ إِنِّى كَانَ لِى قَرِينٌ
37:51
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."

37:52 يَقُولُ أَءِنَّكَ لَمِنَ ٱلْمُصَدِّقِينَ
37:52
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"

37:53 أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَـٰمًا أَءِنَّا لَمَدِينُونَ
37:53
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"

37:54 قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ
37:54
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"

37:55 فَٱطَّلَعَ فَرَءَاهُ فِى سَوَآءِ ٱلْجَحِيمِ
37:55
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.

37:56 قَالَ تَٱللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ
37:56
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."

37:57 وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّى لَكُنتُ مِنَ ٱلْمُحْضَرِينَ
37:57
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."

37:58 أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَ
37:58
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."

37:59 إِلَّا مَوْتَتَنَا ٱلْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ
37:59
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"

37:60 إِنَّ هَـٰذَا لَهُوَ ٱلْفَوْزُ ٱلْعَظِيمُ
37:60
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.

37:61 لِمِثْلِ هَـٰذَا فَلْيَعْمَلِ ٱلْعَـٰمِلُونَ
37:61
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.

37:62 أَذَٰلِكَ خَيْرٌ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ ٱلزَّقُّومِ
37:62
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?

37:63 إِنَّا جَعَلْنَـٰهَا فِتْنَةً لِّلظَّـٰلِمِينَ
37:63
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.

37:64 إِنَّهَا شَجَرَةٌ تَخْرُجُ فِىٓ أَصْلِ ٱلْجَحِيمِ
37:64
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.

37:65 طَلْعُهَا كَأَنَّهُۥ رُءُوسُ ٱلشَّيَـٰطِينِ
37:65
Abubakar Gumi (Hausa) :
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.

37:66 فَإِنَّهُمْ لَـَٔاكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ
37:66
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.

37:67 ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًا مِّنْ حَمِيمٍ
37:67
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.

37:68 ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى ٱلْجَحِيمِ
37:68
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.

37:69 إِنَّهُمْ أَلْفَوْا۟ ءَابَآءَهُمْ ضَآلِّينَ
37:69
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.

37:70 فَهُمْ عَلَىٰٓ ءَاثَـٰرِهِمْ يُهْرَعُونَ
37:70
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.

37:71 وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ ٱلْأَوَّلِينَ
37:71
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.

37:72 وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ
37:72
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.

37:73 فَٱنظُرْ كَيْفَ كَانَ عَـٰقِبَةُ ٱلْمُنذَرِينَ
37:73
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.

37:74 إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ
37:74
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

37:75 وَلَقَدْ نَادَىٰنَا نُوحٌ فَلَنِعْمَ ٱلْمُجِيبُونَ
37:75
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.

37:76 وَنَجَّيْنَـٰهُ وَأَهْلَهُۥ مِنَ ٱلْكَرْبِ ٱلْعَظِيمِ
37:76
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.

37:77 وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُۥ هُمُ ٱلْبَاقِينَ
37:77
Abubakar Gumi (Hausa) :
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.

37:78 وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ
37:78
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.

37:79 سَلَـٰمٌ عَلَىٰ نُوحٍ فِى ٱلْعَـٰلَمِينَ
37:79
Abubakar Gumi (Hausa) :
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.

37:80 إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ
37:80
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

37:81 إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ
37:81
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.

37:82 ثُمَّ أَغْرَقْنَا ٱلْـَٔاخَرِينَ
37:82
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.

37:83 ۞ وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِۦ لَإِبْرَٰهِيمَ
37:83
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.

37:84 إِذْ جَآءَ رَبَّهُۥ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ
37:84
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.

37:85 إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِۦ مَاذَا تَعْبُدُونَ
37:85
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"

37:86 أَئِفْكًا ءَالِهَةً دُونَ ٱللَّهِ تُرِيدُونَ
37:86
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"

37:87 فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
37:87
Abubakar Gumi (Hausa) :
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"

37:88 فَنَظَرَ نَظْرَةً فِى ٱلنُّجُومِ
37:88
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.

37:89 فَقَالَ إِنِّى سَقِيمٌ
37:89
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."

37:90 فَتَوَلَّوْا۟ عَنْهُ مُدْبِرِينَ
37:90
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.

37:91 فَرَاغَ إِلَىٰٓ ءَالِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ
37:91
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?

37:92 مَا لَكُمْ لَا تَنطِقُونَ
37:92
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"

37:93 فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًۢا بِٱلْيَمِينِ
37:93
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.

37:94 فَأَقْبَلُوٓا۟ إِلَيْهِ يَزِفُّونَ
37:94
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.

37:95 قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ
37:95
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,

37:96 وَٱللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ
37:96
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"

37:97 قَالُوا۟ ٱبْنُوا۟ لَهُۥ بُنْيَـٰنًا فَأَلْقُوهُ فِى ٱلْجَحِيمِ
37:97
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."

37:98 فَأَرَادُوا۟ بِهِۦ كَيْدًا فَجَعَلْنَـٰهُمُ ٱلْأَسْفَلِينَ
37:98
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.

37:99 وَقَالَ إِنِّى ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّى سَيَهْدِينِ
37:99
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."

37:100 رَبِّ هَبْ لِى مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ
37:100
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."

37:101 فَبَشَّرْنَـٰهُ بِغُلَـٰمٍ حَلِيمٍ
37:101
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.

37:102 فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ ٱلسَّعْىَ قَالَ يَـٰبُنَىَّ إِنِّىٓ أَرَىٰ فِى ٱلْمَنَامِ أَنِّىٓ أَذْبَحُكَ فَٱنظُرْ مَاذَا تَرَىٰ ۚ قَالَ يَـٰٓأَبَتِ ٱفْعَلْ مَا تُؤْمَرُ ۖ سَتَجِدُنِىٓ إِن شَآءَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلصَّـٰبِرِينَ
37:102
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."

37:103 فَلَمَّآ أَسْلَمَا وَتَلَّهُۥ لِلْجَبِينِ
37:103
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.

37:104 وَنَـٰدَيْنَـٰهُ أَن يَـٰٓإِبْرَٰهِيمُ
37:104
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"

37:105 قَدْ صَدَّقْتَ ٱلرُّءْيَآ ۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ
37:105
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

37:106 إِنَّ هَـٰذَا لَهُوَ ٱلْبَلَـٰٓؤُا۟ ٱلْمُبِينُ
37:106
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.

37:107 وَفَدَيْنَـٰهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍ
37:107
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.

37:108 وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ
37:108
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.

37:109 سَلَـٰمٌ عَلَىٰٓ إِبْرَٰهِيمَ
37:109
Abubakar Gumi (Hausa) :
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.

37:110 كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ
37:110
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

37:111 إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ
37:111
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

37:112 وَبَشَّرْنَـٰهُ بِإِسْحَـٰقَ نَبِيًّا مِّنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ
37:112
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.

37:113 وَبَـٰرَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰٓ إِسْحَـٰقَ ۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌ وَظَالِمٌ لِّنَفْسِهِۦ مُبِينٌ
37:113
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).

37:114 وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَـٰرُونَ
37:114
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.

37:115 وَنَجَّيْنَـٰهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ ٱلْكَرْبِ ٱلْعَظِيمِ
37:115
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.

37:116 وَنَصَرْنَـٰهُمْ فَكَانُوا۟ هُمُ ٱلْغَـٰلِبِينَ
37:116
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.

37:117 وَءَاتَيْنَـٰهُمَا ٱلْكِتَـٰبَ ٱلْمُسْتَبِينَ
37:117
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.

37:118 وَهَدَيْنَـٰهُمَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلْمُسْتَقِيمَ
37:118
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.

37:119 وَتَرَكْنَا عَلَيْهِمَا فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ
37:119
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.

37:120 سَلَـٰمٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَـٰرُونَ
37:120
Abubakar Gumi (Hausa) :
Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.

37:121 إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ
37:121
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

37:122 إِنَّهُمَا مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ
37:122
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.

37:123 وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ
37:123
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

37:124 إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِۦٓ أَلَا تَتَّقُونَ
37:124
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"

37:125 أَتَدْعُونَ بَعْلًا وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ ٱلْخَـٰلِقِينَ
37:125
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"

37:126 ٱللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ
37:126
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"

37:127 فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ
37:127
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).

37:128 إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ
37:128
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

37:129 وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ
37:129
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.

37:130 سَلَـٰمٌ عَلَىٰٓ إِلْ يَاسِينَ
37:130
Abubakar Gumi (Hausa) :
Aminci ya tabbata ga Ilyãs.

37:131 إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ
37:131
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

37:132 إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ
37:132
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

37:133 وَإِنَّ لُوطًا لَّمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ
37:133
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

37:134 إِذْ نَجَّيْنَـٰهُ وَأَهْلَهُۥٓ أَجْمَعِينَ
37:134
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.

37:135 إِلَّا عَجُوزًا فِى ٱلْغَـٰبِرِينَ
37:135
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).

37:136 ثُمَّ دَمَّرْنَا ٱلْـَٔاخَرِينَ
37:136
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.

37:137 وَإِنَّكُمْ لَتَمُرُّونَ عَلَيْهِم مُّصْبِحِينَ
37:137
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.

37:138 وَبِٱلَّيْلِ ۗ أَفَلَا تَعْقِلُونَ
37:138
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?

37:139 وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ
37:139
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

37:140 إِذْ أَبَقَ إِلَى ٱلْفُلْكِ ٱلْمَشْحُونِ
37:140
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.

37:141 فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ ٱلْمُدْحَضِينَ
37:141
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.

37:142 فَٱلْتَقَمَهُ ٱلْحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٌ
37:142
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

37:143 فَلَوْلَآ أَنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلْمُسَبِّحِينَ
37:143
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,

37:144 لَلَبِثَ فِى بَطْنِهِۦٓ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ
37:144
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.

37:145 ۞ فَنَبَذْنَـٰهُ بِٱلْعَرَآءِ وَهُوَ سَقِيمٌ
37:145
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.

37:146 وَأَنۢبَتْنَا عَلَيْهِ شَجَرَةً مِّن يَقْطِينٍ
37:146
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.

37:147 وَأَرْسَلْنَـٰهُ إِلَىٰ مِا۟ئَةِ أَلْفٍ أَوْ يَزِيدُونَ
37:147
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).

37:148 فَـَٔامَنُوا۟ فَمَتَّعْنَـٰهُمْ إِلَىٰ حِينٍ
37:148
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.

37:149 فَٱسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ ٱلْبَنَاتُ وَلَهُمُ ٱلْبَنُونَ
37:149
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"

37:150 أَمْ خَلَقْنَا ٱلْمَلَـٰٓئِكَةَ إِنَـٰثًا وَهُمْ شَـٰهِدُونَ
37:150
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?

37:151 أَلَآ إِنَّهُم مِّنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَ
37:151
Abubakar Gumi (Hausa) :
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.

37:152 وَلَدَ ٱللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَـٰذِبُونَ
37:152
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.

37:153 أَصْطَفَى ٱلْبَنَاتِ عَلَى ٱلْبَنِينَ
37:153
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?

37:154 مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ
37:154
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?

37:155 أَفَلَا تَذَكَّرُونَ
37:155
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, bã ku tunãni?

37:156 أَمْ لَكُمْ سُلْطَـٰنٌ مُّبِينٌ
37:156
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?

37:157 فَأْتُوا۟ بِكِتَـٰبِكُمْ إِن كُنتُمْ صَـٰدِقِينَ
37:157
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.

37:158 وَجَعَلُوا۟ بَيْنَهُۥ وَبَيْنَ ٱلْجِنَّةِ نَسَبًا ۚ وَلَقَدْ عَلِمَتِ ٱلْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ
37:158
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"

37:159 سُبْحَـٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ
37:159
Abubakar Gumi (Hausa) :
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.

37:160 إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ
37:160
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

37:161 فَإِنَّكُمْ وَمَا تَعْبُدُونَ
37:161
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,

37:162 مَآ أَنتُمْ عَلَيْهِ بِفَـٰتِنِينَ
37:162
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.

37:163 إِلَّا مَنْ هُوَ صَالِ ٱلْجَحِيمِ
37:163
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.

37:164 وَمَا مِنَّآ إِلَّا لَهُۥ مَقَامٌ مَّعْلُومٌ
37:164
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."

37:165 وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلصَّآفُّونَ
37:165
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."

37:166 وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلْمُسَبِّحُونَ
37:166
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."

37:167 وَإِن كَانُوا۟ لَيَقُولُونَ
37:167
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,

37:168 لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًا مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ
37:168
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."

37:169 لَكُنَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ
37:169
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."

37:170 فَكَفَرُوا۟ بِهِۦ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ
37:170
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.

37:171 وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا ٱلْمُرْسَلِينَ
37:171
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.

37:172 إِنَّهُمْ لَهُمُ ٱلْمَنصُورُونَ
37:172
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.

37:173 وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ ٱلْغَـٰلِبُونَ
37:173
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.

37:174 فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ
37:174
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.

37:175 وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ
37:175
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.

37:176 أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ
37:176
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?

37:177 فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَآءَ صَبَاحُ ٱلْمُنذَرِينَ
37:177
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.

37:178 وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ
37:178
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.

37:179 وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ
37:179
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.

37:180 سُبْحَـٰنَ رَبِّكَ رَبِّ ٱلْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ
37:180
Abubakar Gumi (Hausa) :
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.

37:181 وَسَلَـٰمٌ عَلَى ٱلْمُرْسَلِينَ
37:181
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.

37:182 وَٱلْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
37:182
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.