Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

75 Al-Qiyāmah ٱلْقِيَامَة

< Previous   40 Āyah   The Resurrection      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

75:1 لَآ أُقْسِمُ بِيَوْمِ ٱلْقِيَـٰمَةِ
75:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.

75:2 وَلَآ أُقْسِمُ بِٱلنَّفْسِ ٱللَّوَّامَةِ
75:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.

75:3 أَيَحْسَبُ ٱلْإِنسَـٰنُ أَلَّن نَّجْمَعَ عِظَامَهُۥ
75:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?

75:4 بَلَىٰ قَـٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّىَ بَنَانَهُۥ
75:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.

75:5 بَلْ يُرِيدُ ٱلْإِنسَـٰنُ لِيَفْجُرَ أَمَامَهُۥ
75:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.

75:6 يَسْـَٔلُ أَيَّانَ يَوْمُ ٱلْقِيَـٰمَةِ
75:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"

75:7 فَإِذَا بَرِقَ ٱلْبَصَرُ
75:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).

75:8 وَخَسَفَ ٱلْقَمَرُ
75:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).

75:9 وَجُمِعَ ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ
75:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Aka tãra rãnã da watã

75:10 يَقُولُ ٱلْإِنسَـٰنُ يَوْمَئِذٍ أَيْنَ ٱلْمَفَرُّ
75:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"

75:11 كَلَّا لَا وَزَرَ
75:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! bãbu mafaka.

75:12 إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ ٱلْمُسْتَقَرُّ
75:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.

75:13 يُنَبَّؤُا۟ ٱلْإِنسَـٰنُ يَوْمَئِذٍۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ
75:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.

75:14 بَلِ ٱلْإِنسَـٰنُ عَلَىٰ نَفْسِهِۦ بَصِيرَةٌ
75:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.

75:15 وَلَوْ أَلْقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ
75:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).

75:16 لَا تُحَرِّكْ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعْجَلَ بِهِۦٓ
75:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).

75:17 إِنَّ عَلَيْنَا جَمْعَهُۥ وَقُرْءَانَهُۥ
75:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.

75:18 فَإِذَا قَرَأْنَـٰهُ فَٱتَّبِعْ قُرْءَانَهُۥ
75:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.

75:19 ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا بَيَانَهُۥ
75:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.

75:20 كَلَّا بَلْ تُحِبُّونَ ٱلْعَاجِلَةَ
75:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.

75:21 وَتَذَرُونَ ٱلْـَٔاخِرَةَ
75:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).

75:22 وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاضِرَةٌ
75:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.

75:23 إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٌ
75:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.

75:24 وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍۭ بَاسِرَةٌ
75:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.

75:25 تَظُنُّ أَن يُفْعَلَ بِهَا فَاقِرَةٌ
75:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.

75:26 كَلَّآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلتَّرَاقِىَ
75:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.

75:27 وَقِيلَ مَنْ ۜ رَاقٍ
75:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"

75:28 وَظَنَّ أَنَّهُ ٱلْفِرَاقُ
75:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.

75:29 وَٱلْتَفَّتِ ٱلسَّاقُ بِٱلسَّاقِ
75:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.

75:30 إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ ٱلْمَسَاقُ
75:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.

75:31 فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ
75:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!

75:32 وَلَـٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
75:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!

75:33 ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ يَتَمَطَّىٰٓ
75:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.

75:34 أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ
75:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.

75:35 ثُمَّ أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰٓ
75:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.

75:36 أَيَحْسَبُ ٱلْإِنسَـٰنُ أَن يُتْرَكَ سُدًى
75:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?

75:37 أَلَمْ يَكُ نُطْفَةً مِّن مَّنِىٍّ يُمْنَىٰ
75:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)

75:38 ثُمَّ كَانَ عَلَقَةً فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ
75:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;

75:39 فَجَعَلَ مِنْهُ ٱلزَّوْجَيْنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰٓ
75:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?

75:40 أَلَيْسَ ذَٰلِكَ بِقَـٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يُحْـِۧىَ ٱلْمَوْتَىٰ
75:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?