Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

88 Al-Ghāshiyah ٱلْغَاشِيَة

< Previous   26 Āyah   The Overwhelming      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

88:1 هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلْغَـٰشِيَةِ
88:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne labãrin (¡iyãma) mai rufe mutãne da tsoronta yã zo maka?

88:2 وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ خَـٰشِعَةٌ
88:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wasu huskõki a rãnar nan ƙasƙantattu ne.

88:3 عَامِلَةٌ نَّاصِبَةٌ
88:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mãsu aikin wahala ne, mãsu gajiya.

88:4 تَصْلَىٰ نَارًا حَامِيَةً
88:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Zã su shiga wata wuta mai zãfi.

88:5 تُسْقَىٰ مِنْ عَيْنٍ ءَانِيَةٍ
88:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ana shãyar da su daga wani marmaro mai zãfin ruwa.

88:6 لَّيْسَ لَهُمْ طَعَامٌ إِلَّا مِن ضَرِيعٍ
88:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ba su da wani abinci fãce dai daga danyi.

88:7 لَّا يُسْمِنُ وَلَا يُغْنِى مِن جُوعٍ
88:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã ya sanya ƙiba, kuma bã zai wadãtar daga yunwa ba.

88:8 وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاعِمَةٌ
88:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wasu huskõki a rãnar nan mãsu ni'ima ne.

88:9 لِّسَعْيِهَا رَاضِيَةٌ
88:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Game da aikinsu, masu yarda ne.

88:10 فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍ
88:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Suna) a cikin Aljanna maɗaukakiya.

88:11 لَّا تَسْمَعُ فِيهَا لَـٰغِيَةً
88:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã zã su ji yãsassar magana ba, a cikinta.

88:12 فِيهَا عَيْنٌ جَارِيَةٌ
88:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikinta akwai marmaro mai gudãna.

88:13 فِيهَا سُرُرٌ مَّرْفُوعَةٌ
88:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikinta akwai gadãje maɗaukaka.

88:14 وَأَكْوَابٌ مَّوْضُوعَةٌ
88:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da kõfuna ar'aje.

88:15 وَنَمَارِقُ مَصْفُوفَةٌ
88:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da filõli jẽre,

88:16 وَزَرَابِىُّ مَبْثُوثَةٌ
88:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da katifu shimfiɗe.

88:17 أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلْإِبِلِ كَيْفَ خُلِقَتْ
88:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe to bã zã su dũbãwa ba ga rãƙumã yadda aka halitta su?

88:18 وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيْفَ رُفِعَتْ
88:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da zuwa ga sama yadda aka ɗaukaka ta?

88:19 وَإِلَى ٱلْجِبَالِ كَيْفَ نُصِبَتْ
88:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da zuwa ga duwãtsu yadda aka kafa su?

88:20 وَإِلَى ٱلْأَرْضِ كَيْفَ سُطِحَتْ
88:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da zuwa ga ƙasa yadda aka shimfiɗã ta?

88:21 فَذَكِّرْ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٌ
88:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
sabõda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai.

88:22 لَّسْتَ عَلَيْهِم بِمُصَيْطِرٍ
88:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ba ka zama mai ĩkon tanƙwasãwa a kansu ba.

88:23 إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ
88:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fãce dai duk wanda ya jũya bãya, kuma ya kãfirta.

88:24 فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَكْبَرَ
88:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, Allah zai yi masa azãba, azãbar nan da take mafi girma.

88:25 إِنَّ إِلَيْنَآ إِيَابَهُمْ
88:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, zuwa gare Mu kõmõwarsu take.

88:26 ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا حِسَابَهُم
88:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisãbi.