Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

100 Al-`Ādiyāt ٱلْعَادِيَات

< Previous   11 Āyah   The Courser      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

100:1 وَٱلْعَـٰدِيَـٰتِ ضَبْحًا
100:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ina rantsuwa da dawãki mãsu gudu suna fitar da kũkan ciki.

100:2 فَٱلْمُورِيَـٰتِ قَدْحًا
100:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mãsu ƙyasta wuta (da kõfatansu a kan duwatsu) ƙyastawa.

100:3 فَٱلْمُغِيرَٰتِ صُبْحًا
100:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan mãsu yin hari a lokacin asuba.

100:4 فَأَثَرْنَ بِهِۦ نَقْعًا
100:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai su motsar da ƙũra game da shi.

100:5 فَوَسَطْنَ بِهِۦ جَمْعًا
100:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai su shiga, game da ita (ƙũrar), a tsakãnin jama'ar maƙiya.

100:6 إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ لِرَبِّهِۦ لَكَنُودٌ
100:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijinsa.

100:7 وَإِنَّهُۥ عَلَىٰ ذَٰلِكَ لَشَهِيدٌ
100:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne shi mai shaida ne a kan laifinsa dl haka.

100:8 وَإِنَّهُۥ لِحُبِّ ٱلْخَيْرِ لَشَدِيدٌ
100:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma 1alle ne ga dũkiya shi mai tsananin so ne.

100:9 ۞ أَفَلَا يَعْلَمُ إِذَا بُعْثِرَ مَا فِى ٱلْقُبُورِ
100:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, bã ya da sanin lõkacin da aka tõne abin da yake cikin kaburbura.

100:10 وَحُصِّلَ مَا فِى ٱلصُّدُورِ
100:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Aka bayyana abin da ke cikin zukata.

100:11 إِنَّ رَبَّهُم بِهِمْ يَوْمَئِذٍ لَّخَبِيرٌۢ
100:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne Ubangijinsu, game da su a ranar nan Mai ƙididdigewa ne?