Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

74 Al-Muddaththir ٱلْمُدَّثِّر

< Previous   56 Āyah   The Cloaked One      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

74:1 يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْمُدَّثِّرُ
74:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.

74:2 قُمْ فَأَنذِرْ
74:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi

74:3 وَرَبَّكَ فَكَبِّرْ
74:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,

74:4 وَثِيَابَكَ فَطَهِّرْ
74:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,

74:5 وَٱلرُّجْزَ فَٱهْجُرْ
74:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.

74:6 وَلَا تَمْنُن تَسْتَكْثِرُ
74:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri

74:7 وَلِرَبِّكَ فَٱصْبِرْ
74:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure

74:8 فَإِذَا نُقِرَ فِى ٱلنَّاقُورِ
74:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.

74:9 فَذَٰلِكَ يَوْمَئِذٍ يَوْمٌ عَسِيرٌ
74:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya

74:10 عَلَى ٱلْكَـٰفِرِينَ غَيْرُ يَسِيرٍ
74:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.

74:11 ذَرْنِى وَمَنْ خَلَقْتُ وَحِيدًا
74:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,

74:12 وَجَعَلْتُ لَهُۥ مَالًا مَّمْدُودًا
74:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya

74:13 وَبَنِينَ شُهُودًا
74:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da ɗiyã halartattu,

74:14 وَمَهَّدتُّ لَهُۥ تَمْهِيدًا
74:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.

74:15 ثُمَّ يَطْمَعُ أَنْ أَزِيدَ
74:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!

74:16 كَلَّآ ۖ إِنَّهُۥ كَانَ لِـَٔايَـٰتِنَا عَنِيدًا
74:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyinMu, mai tsaurin kai.

74:17 سَأُرْهِقُهُۥ صَعُودًا
74:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.

74:18 إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ
74:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)

74:19 فَقُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ
74:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.

74:20 ثُمَّ قُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ
74:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.

74:21 ثُمَّ نَظَرَ
74:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, ya yi tunãni

74:22 ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ
74:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.

74:23 ثُمَّ أَدْبَرَ وَٱسْتَكْبَرَ
74:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,

74:24 فَقَالَ إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا سِحْرٌ يُؤْثَرُ
74:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."

74:25 إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا قَوْلُ ٱلْبَشَرِ
74:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Wannan maganar mutum dai ce."

74:26 سَأُصْلِيهِ سَقَرَ
74:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.

74:27 وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سَقَرُ
74:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!

74:28 لَا تُبْقِى وَلَا تَذَرُ
74:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.

74:29 لَوَّاحَةٌ لِّلْبَشَرِ
74:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).

74:30 عَلَيْهَا تِسْعَةَ عَشَرَ
74:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.

74:31 وَمَا جَعَلْنَآ أَصْحَـٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةً ۙ وَمَا جَعَلْنَا عِدَّتَهُمْ إِلَّا فِتْنَةً لِّلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لِيَسْتَيْقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَـٰبَ وَيَزْدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓا۟ إِيمَـٰنًا ۙ وَلَا يَرْتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَـٰبَ وَٱلْمُؤْمِنُونَ ۙ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِى قُلُوبِهِم مَّرَضٌ وَٱلْكَـٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَـٰذَا مَثَلًا ۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهْدِى مَن يَشَآءُ ۚ وَمَا يَعْلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَ ۚ وَمَا هِىَ إِلَّا ذِكْرَىٰ لِلْبَشَرِ
74:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.

74:32 كَلَّا وَٱلْقَمَرِ
74:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Ina rantsuwa da watã.

74:33 وَٱلَّيْلِ إِذْ أَدْبَرَ
74:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.

74:34 وَٱلصُّبْحِ إِذَآ أَسْفَرَ
74:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da sãfiya idan ta wãye.

74:35 إِنَّهَا لَإِحْدَى ٱلْكُبَرِ
74:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.

74:36 نَذِيرًا لِّلْبَشَرِ
74:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai gargaɗĩ ce ga mutum.

74:37 لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَتَقَدَّمَ أَوْ يَتَأَخَّرَ
74:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.

74:38 كُلُّ نَفْسٍۭ بِمَا كَسَبَتْ رَهِينَةٌ
74:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.

74:39 إِلَّآ أَصْحَـٰبَ ٱلْيَمِينِ
74:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fãce mutãnen dãma.

74:40 فِى جَنَّـٰتٍ يَتَسَآءَلُونَ
74:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikin Aljanna suna tambayar jũna.

74:41 عَنِ ٱلْمُجْرِمِينَ
74:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
Game da mãsu laifi.

74:42 مَا سَلَكَكُمْ فِى سَقَرَ
74:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"

74:43 قَالُوا۟ لَمْ نَكُ مِنَ ٱلْمُصَلِّينَ
74:43
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."

74:44 وَلَمْ نَكُ نُطْعِمُ ٱلْمِسْكِينَ
74:44
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."

74:45 وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلْخَآئِضِينَ
74:45
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."

74:46 وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ
74:46
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."

74:47 حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلْيَقِينُ
74:47
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."

74:48 فَمَا تَنفَعُهُمْ شَفَـٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ
74:48
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.

74:49 فَمَا لَهُمْ عَنِ ٱلتَّذْكِرَةِ مُعْرِضِينَ
74:49
Abubakar Gumi (Hausa) :
Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.

74:50 كَأَنَّهُمْ حُمُرٌ مُّسْتَنفِرَةٌ
74:50
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.

74:51 فَرَّتْ مِن قَسْوَرَةٍۭ
74:51
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sun gudu daga zãki.

74:52 بَلْ يُرِيدُ كُلُّ ٱمْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُؤْتَىٰ صُحُفًا مُّنَشَّرَةً
74:52
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa

74:53 كَلَّا ۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلْـَٔاخِرَةَ
74:53
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.

74:54 كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذْكِرَةٌ
74:54
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.

74:55 فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ
74:55
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dõmin wanda ya so, ya tuna.

74:56 وَمَا يَذْكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ ۚ هُوَ أَهْلُ ٱلتَّقْوَىٰ وَأَهْلُ ٱلْمَغْفِرَةِ
74:56
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.