Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

81 At-Takwīr ٱلتَّكْوِير

< Previous   29 Āyah   The Overthrowing      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

81:1 إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ
81:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Idan rãna aka shafe haskenta

81:2 وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ
81:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

81:3 وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ
81:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

81:4 وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ
81:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

81:5 وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ
81:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

81:6 وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ
81:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

81:7 وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ
81:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.

81:8 وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ
81:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.

81:9 بِأَىِّ ذَنۢبٍ قُتِلَتْ
81:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

81:10 وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ
81:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

81:11 وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ
81:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.

81:12 وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ
81:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta

81:13 وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ
81:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

81:14 عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّآ أَحْضَرَتْ
81:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

81:15 فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ
81:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.

81:16 ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ
81:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mãsu gudu suna ɓũya.

81:17 وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ
81:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da dare idan ya bãyar da bãya.

81:18 وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ
81:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.

81:19 إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
81:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

81:20 ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍ
81:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

81:21 مُّطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ
81:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

81:22 وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ
81:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

81:23 وَلَقَدْ رَءَاهُ بِٱلْأُفُقِ ٱلْمُبِينِ
81:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.

81:24 وَمَا هُوَ عَلَى ٱلْغَيْبِ بِضَنِينٍ
81:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.

81:25 وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَـٰنٍ رَّجِيمٍ
81:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

81:26 فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ
81:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, a inã zã ku tafi?

81:27 إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَـٰلَمِينَ
81:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

81:28 لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ
81:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

81:29 وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
81:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.