Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

81 At-Takwīr ٱلتَّكْوِير

< Previous   29 Āyah   The Overthrowing      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

81:1 إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ
81:1 Idan rãna aka shafe haskenta - Abubakar Gumi (Hausa)

81:2 وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ
81:2 Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani). - Abubakar Gumi (Hausa)

81:3 وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ
81:3 Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:4 وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ
81:4 Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:5 وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ
81:5 Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:6 وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ
81:6 Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:7 وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ
81:7 Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:8 وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ
81:8 Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:9 بِأَىِّ ذَنۢبٍ قُتِلَتْ
81:9 "Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?" - Abubakar Gumi (Hausa)

81:10 وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ
81:10 Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su). - Abubakar Gumi (Hausa)

81:11 وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ
81:11 Kuma idan sama aka fẽɗe ta. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:12 وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ
81:12 Kuma idan Jahĩm aka hũra ta - Abubakar Gumi (Hausa)

81:13 وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ
81:13 Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:14 عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّآ أَحْضَرَتْ
81:14 Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan). - Abubakar Gumi (Hausa)

81:15 فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ
81:15 To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:16 ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ
81:16 Mãsu gudu suna ɓũya. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:17 وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ
81:17 Da dare idan ya bãyar da bãya. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:18 وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ
81:18 Da sãfiya idan ta yi lumfashi. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:19 إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
81:19 Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:20 ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍ
81:20 Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:21 مُّطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ
81:21 Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:22 وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ
81:22 Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:23 وَلَقَدْ رَءَاهُ بِٱلْأُفُقِ ٱلْمُبِينِ
81:23 Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:24 وَمَا هُوَ عَلَى ٱلْغَيْبِ بِضَنِينٍ
81:24 Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:25 وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَـٰنٍ رَّجِيمٍ
81:25 Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:26 فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ
81:26 Shin, a inã zã ku tafi? - Abubakar Gumi (Hausa)

81:27 إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَـٰلَمِينَ
81:27 Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:28 لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ
81:28 Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu. - Abubakar Gumi (Hausa)

81:29 وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
81:29 Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda. - Abubakar Gumi (Hausa)