Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
81:1
إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ
81:1
Idan rãna aka shafe haskenta - Abubakar Gumi (Hausa)
81:2
وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ
81:2
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani). - Abubakar Gumi (Hausa)
81:3
وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ
81:3
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:4
وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ
81:4
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:5
وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ
81:5
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:6
وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ
81:6
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:7
وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ
81:7
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:8
وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ
81:8
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:9
بِأَىِّ ذَنۢبٍ قُتِلَتْ
81:9
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?" - Abubakar Gumi (Hausa)
81:10
وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ
81:10
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su). - Abubakar Gumi (Hausa)
81:11
وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ
81:11
Kuma idan sama aka fẽɗe ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:12
وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ
81:12
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta - Abubakar Gumi (Hausa)
81:13
وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ
81:13
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:14
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّآ أَحْضَرَتْ
81:14
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan). - Abubakar Gumi (Hausa)
81:15
فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ
81:15
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:16
ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ
81:16
Mãsu gudu suna ɓũya. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:17
وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ
81:17
Da dare idan ya bãyar da bãya. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:18
وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ
81:18
Da sãfiya idan ta yi lumfashi. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:19
إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
81:19
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:20
ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍ
81:20
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:21
مُّطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ
81:21
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:22
وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ
81:22
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:23
وَلَقَدْ رَءَاهُ بِٱلْأُفُقِ ٱلْمُبِينِ
81:23
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:24
وَمَا هُوَ عَلَى ٱلْغَيْبِ بِضَنِينٍ
81:24
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:25
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَـٰنٍ رَّجِيمٍ
81:25
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:26
فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ
81:26
Shin, a inã zã ku tafi? - Abubakar Gumi (Hausa)
81:27
إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَـٰلَمِينَ
81:27
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:28
لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ
81:28
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu. - Abubakar Gumi (Hausa)
81:29
وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
81:29
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda. - Abubakar Gumi (Hausa)