Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

93 Ađ-Đuĥaá ٱلضُّحَىٰ

< Previous   11 Āyah   The Morning Hours      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

93:1 وَٱلضُّحَىٰ
93:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Inã rantsuwa da hantsi.

93:2 وَٱلَّيْلِ إِذَا سَجَىٰ
93:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).

93:3 مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ
93:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.

93:4 وَلَلْـَٔاخِرَةُ خَيْرٌ لَّكَ مِنَ ٱلْأُولَىٰ
93:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.

93:5 وَلَسَوْفَ يُعْطِيكَ رَبُّكَ فَتَرْضَىٰٓ
93:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.

93:6 أَلَمْ يَجِدْكَ يَتِيمًا فَـَٔاوَىٰ
93:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?

93:7 وَوَجَدَكَ ضَآلًّا فَهَدَىٰ
93:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?

93:8 وَوَجَدَكَ عَآئِلًا فَأَغْنَىٰ
93:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?

93:9 فَأَمَّا ٱلْيَتِيمَ فَلَا تَقْهَرْ
93:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.

93:10 وَأَمَّا ٱلسَّآئِلَ فَلَا تَنْهَرْ
93:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.

93:11 وَأَمَّا بِنِعْمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثْ
93:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).