Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

55 Ar-Raĥmān ٱلرَّحْمَٰن

< Previous   78 Āyah   The Beneficent      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

55:1 ٱلرَّحْمَـٰنُ
55:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Allah) Mai rahama.

55:2 عَلَّمَ ٱلْقُرْءَانَ
55:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yã sanar da Alƙur'ani.

55:3 خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ
55:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yã halitta mutum.

55:4 عَلَّمَهُ ٱلْبَيَانَ
55:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yã sanar da shi bayãni (magana).

55:5 ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ بِحُسْبَانٍ
55:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.

55:6 وَٱلنَّجْمُ وَٱلشَّجَرُ يَسْجُدَانِ
55:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.

55:7 وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلْمِيزَانَ
55:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.

55:8 أَلَّا تَطْغَوْا۟ فِى ٱلْمِيزَانِ
55:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.

55:9 وَأَقِيمُوا۟ ٱلْوَزْنَ بِٱلْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا۟ ٱلْمِيزَانَ
55:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.

55:10 وَٱلْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ
55:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.

55:11 فِيهَا فَـٰكِهَةٌ وَٱلنَّخْلُ ذَاتُ ٱلْأَكْمَامِ
55:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.

55:12 وَٱلْحَبُّ ذُو ٱلْعَصْفِ وَٱلرَّيْحَانُ
55:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.

55:13 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?

55:14 خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ مِن صَلْصَـٰلٍ كَٱلْفَخَّارِ
55:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.

55:15 وَخَلَقَ ٱلْجَآنَّ مِن مَّارِجٍ مِّن نَّارٍ
55:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.

55:16 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:17 رَبُّ ٱلْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ ٱلْمَغْرِبَيْنِ
55:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.

55:18 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:19 مَرَجَ ٱلْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ
55:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.

55:20 بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌ لَّا يَبْغِيَانِ
55:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.

55:21 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:22 يَخْرُجُ مِنْهُمَا ٱللُّؤْلُؤُ وَٱلْمَرْجَانُ
55:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.

55:23 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:24 وَلَهُ ٱلْجَوَارِ ٱلْمُنشَـَٔاتُ فِى ٱلْبَحْرِ كَٱلْأَعْلَـٰمِ
55:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.

55:25 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:26 كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍ
55:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.

55:27 وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو ٱلْجَلَـٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ
55:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.

55:28 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:29 يَسْـَٔلُهُۥ مَن فِى ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِى شَأْنٍ
55:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.

55:30 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:31 سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ
55:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!

55:32 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:33 يَـٰمَعْشَرَ ٱلْجِنِّ وَٱلْإِنسِ إِنِ ٱسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا۟ مِنْ أَقْطَارِ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ فَٱنفُذُوا۟ ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَـٰنٍ
55:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.

55:34 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:35 يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌ مِّن نَّارٍ وَنُحَاسٌ فَلَا تَنتَصِرَانِ
55:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?

55:36 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:37 فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ وَرْدَةً كَٱلدِّهَانِ
55:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.

55:38 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:39 فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُسْـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٌ وَلَا جَآنٌّ
55:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.

55:40 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:41 يُعْرَفُ ٱلْمُجْرِمُونَ بِسِيمَـٰهُمْ فَيُؤْخَذُ بِٱلنَّوَٰصِى وَٱلْأَقْدَامِ
55:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.

55:42 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:43 هَـٰذِهِۦ جَهَنَّمُ ٱلَّتِى يُكَذِّبُ بِهَا ٱلْمُجْرِمُونَ
55:43
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.

55:44 يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ ءَانٍ
55:44
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.

55:45 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:45
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:46 وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ
55:46
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.

55:47 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:47
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:48 ذَوَاتَآ أَفْنَانٍ
55:48
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mãsu rassan itãce.

55:49 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:49
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:50 فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ
55:50
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.

55:51 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:51
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:52 فِيهِمَا مِن كُلِّ فَـٰكِهَةٍ زَوْجَانِ
55:52
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.

55:53 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:53
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:54 مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ فُرُشٍۭ بَطَآئِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍ ۚ وَجَنَى ٱلْجَنَّتَيْنِ دَانٍ
55:54
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.

55:55 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:55
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:56 فِيهِنَّ قَـٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّ
55:56
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.

55:57 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:57
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:58 كَأَنَّهُنَّ ٱلْيَاقُوتُ وَٱلْمَرْجَانُ
55:58
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.

55:59 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:59
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:60 هَلْ جَزَآءُ ٱلْإِحْسَـٰنِ إِلَّا ٱلْإِحْسَـٰنُ
55:60
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.

55:61 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:61
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:62 وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ
55:62
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.

55:63 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:63
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:64 مُدْهَآمَّتَانِ
55:64
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mãsu duhun inuwa.

55:65 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:65
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:66 فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ
55:66
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.

55:67 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:67
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:68 فِيهِمَا فَـٰكِهَةٌ وَنَخْلٌ وَرُمَّانٌ
55:68
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.

55:69 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:69
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:70 فِيهِنَّ خَيْرَٰتٌ حِسَانٌ
55:70
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.

55:71 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:71
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:72 حُورٌ مَّقْصُورَٰتٌ فِى ٱلْخِيَامِ
55:72
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.

55:73 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:73
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:74 لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّ
55:74
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.

55:75 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:75
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:76 مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍ وَعَبْقَرِىٍّ حِسَانٍ
55:76
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.

55:77 فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:77
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

55:78 تَبَـٰرَكَ ٱسْمُ رَبِّكَ ذِى ٱلْجَلَـٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ
55:78
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.