Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
55:1
ٱلرَّحْمَـٰنُ
55:1
(Allah) Mai rahama. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:2
عَلَّمَ ٱلْقُرْءَانَ
55:2
Yã sanar da Alƙur'ani. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:3
خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ
55:3
Yã halitta mutum. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:4
عَلَّمَهُ ٱلْبَيَانَ
55:4
Yã sanar da shi bayãni (magana). - Abubakar Gumi (Hausa)
55:5
ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ بِحُسْبَانٍ
55:5
Rãnã da watã a kan lissãfi suke. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:6
وَٱلنَّجْمُ وَٱلشَّجَرُ يَسْجُدَانِ
55:6
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:7
وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلْمِيزَانَ
55:7
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:8
أَلَّا تَطْغَوْا۟ فِى ٱلْمِيزَانِ
55:8
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:9
وَأَقِيمُوا۟ ٱلْوَزْنَ بِٱلْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا۟ ٱلْمِيزَانَ
55:9
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:10
وَٱلْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ
55:10
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:11
فِيهَا فَـٰكِهَةٌ وَٱلنَّخْلُ ذَاتُ ٱلْأَكْمَامِ
55:11
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:12
وَٱلْحَبُّ ذُو ٱلْعَصْفِ وَٱلرَّيْحَانُ
55:12
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:13
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:13
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:14
خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ مِن صَلْصَـٰلٍ كَٱلْفَخَّارِ
55:14
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:15
وَخَلَقَ ٱلْجَآنَّ مِن مَّارِجٍ مِّن نَّارٍ
55:15
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:16
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:16
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:17
رَبُّ ٱلْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ ٱلْمَغْرِبَيْنِ
55:17
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:18
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:18
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:19
مَرَجَ ٱلْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ
55:19
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:20
بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌ لَّا يَبْغِيَانِ
55:20
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:21
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:21
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:22
يَخْرُجُ مِنْهُمَا ٱللُّؤْلُؤُ وَٱلْمَرْجَانُ
55:22
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:23
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:23
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:24
وَلَهُ ٱلْجَوَارِ ٱلْمُنشَـَٔاتُ فِى ٱلْبَحْرِ كَٱلْأَعْلَـٰمِ
55:24
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:25
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:25
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:26
كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍ
55:26
Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:27
وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو ٱلْجَلَـٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ
55:27
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:28
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:28
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:29
يَسْـَٔلُهُۥ مَن فِى ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِى شَأْنٍ
55:29
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:30
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:30
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:31
سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ
55:31
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu! - Abubakar Gumi (Hausa)
55:32
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:32
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:33
يَـٰمَعْشَرَ ٱلْجِنِّ وَٱلْإِنسِ إِنِ ٱسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا۟ مِنْ أَقْطَارِ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ فَٱنفُذُوا۟ ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَـٰنٍ
55:33
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:34
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:34
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:35
يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌ مِّن نَّارٍ وَنُحَاسٌ فَلَا تَنتَصِرَانِ
55:35
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:36
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:36
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:37
فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ وَرْدَةً كَٱلدِّهَانِ
55:37
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:38
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:38
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:39
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُسْـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٌ وَلَا جَآنٌّ
55:39
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:40
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:40
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:41
يُعْرَفُ ٱلْمُجْرِمُونَ بِسِيمَـٰهُمْ فَيُؤْخَذُ بِٱلنَّوَٰصِى وَٱلْأَقْدَامِ
55:41
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:42
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:42
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:43
هَـٰذِهِۦ جَهَنَّمُ ٱلَّتِى يُكَذِّبُ بِهَا ٱلْمُجْرِمُونَ
55:43
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:44
يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ ءَانٍ
55:44
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:45
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:45
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:46
وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ
55:46
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:47
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:47
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:48
ذَوَاتَآ أَفْنَانٍ
55:48
Mãsu rassan itãce. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:49
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:49
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:50
فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ
55:50
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:51
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:51
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:52
فِيهِمَا مِن كُلِّ فَـٰكِهَةٍ زَوْجَانِ
55:52
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:53
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:53
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:54
مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ فُرُشٍۭ بَطَآئِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍ ۚ وَجَنَى ٱلْجَنَّتَيْنِ دَانٍ
55:54
Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:55
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:55
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:56
فِيهِنَّ قَـٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّ
55:56
A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:57
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:57
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:58
كَأَنَّهُنَّ ٱلْيَاقُوتُ وَٱلْمَرْجَانُ
55:58
Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:59
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:59
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:60
هَلْ جَزَآءُ ٱلْإِحْسَـٰنِ إِلَّا ٱلْإِحْسَـٰنُ
55:60
Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:61
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:61
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:62
وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ
55:62
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:63
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:63
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:64
مُدْهَآمَّتَانِ
55:64
Mãsu duhun inuwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:65
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:65
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:66
فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ
55:66
A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:67
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:67
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:68
فِيهِمَا فَـٰكِهَةٌ وَنَخْلٌ وَرُمَّانٌ
55:68
A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:69
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:69
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:70
فِيهِنَّ خَيْرَٰتٌ حِسَانٌ
55:70
A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:71
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:71
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:72
حُورٌ مَّقْصُورَٰتٌ فِى ٱلْخِيَامِ
55:72
Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:73
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:73
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:74
لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّ
55:74
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:75
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:75
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:76
مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍ وَعَبْقَرِىٍّ حِسَانٍ
55:76
Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
55:77
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
55:77
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
55:78
تَبَـٰرَكَ ٱسْمُ رَبِّكَ ذِى ٱلْجَلَـٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ
55:78
Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka. - Abubakar Gumi (Hausa)