Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

68 Al-Qalam ٱلْقَلَم

< Previous   52 Āyah   The Pen      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

68:1 نٓ ۚ وَٱلْقَلَمِ وَمَا يَسْطُرُونَ
68:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.

68:2 مَآ أَنتَ بِنِعْمَةِ رَبِّكَ بِمَجْنُونٍ
68:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.

68:3 وَإِنَّ لَكَ لَأَجْرًا غَيْرَ مَمْنُونٍ
68:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.

68:4 وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٍ
68:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.

68:5 فَسَتُبْصِرُ وَيُبْصِرُونَ
68:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.

68:6 بِأَييِّكُمُ ٱلْمَفْتُونُ
68:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ga wanenku haukã take.

68:7 إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعْلَمُ بِٱلْمُهْتَدِينَ
68:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.

68:8 فَلَا تُطِعِ ٱلْمُكَذِّبِينَ
68:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.

68:9 وَدُّوا۟ لَوْ تُدْهِنُ فَيُدْهِنُونَ
68:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.

68:10 وَلَا تُطِعْ كُلَّ حَلَّافٍ مَّهِينٍ
68:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.

68:11 هَمَّازٍ مَّشَّآءٍۭ بِنَمِيمٍ
68:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.

68:12 مَّنَّاعٍ لِّلْخَيْرِ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ
68:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.

68:13 عُتُلٍّۭ بَعْدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ
68:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).

68:14 أَن كَانَ ذَا مَالٍ وَبَنِينَ
68:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.

68:15 إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَـٰتُنَا قَالَ أَسَـٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ
68:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."

68:16 سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلْخُرْطُومِ
68:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.

68:17 إِنَّا بَلَوْنَـٰهُمْ كَمَا بَلَوْنَآ أَصْحَـٰبَ ٱلْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا۟ لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَ
68:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.

68:18 وَلَا يَسْتَثْنُونَ
68:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.

68:19 فَطَافَ عَلَيْهَا طَآئِفٌ مِّن رَّبِّكَ وَهُمْ نَآئِمُونَ
68:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.

68:20 فَأَصْبَحَتْ كَٱلصَّرِيمِ
68:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.

68:21 فَتَنَادَوْا۟ مُصْبِحِينَ
68:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.

68:22 أَنِ ٱغْدُوا۟ عَلَىٰ حَرْثِكُمْ إِن كُنتُمْ صَـٰرِمِينَ
68:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.

68:23 فَٱنطَلَقُوا۟ وَهُمْ يَتَخَـٰفَتُونَ
68:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).

68:24 أَن لَّا يَدْخُلَنَّهَا ٱلْيَوْمَ عَلَيْكُم مِّسْكِينٌ
68:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"

68:25 وَغَدَوْا۟ عَلَىٰ حَرْدٍ قَـٰدِرِينَ
68:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.

68:26 فَلَمَّا رَأَوْهَا قَالُوٓا۟ إِنَّا لَضَآلُّونَ
68:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"

68:27 بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ
68:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."

68:28 قَالَ أَوْسَطُهُمْ أَلَمْ أَقُل لَّكُمْ لَوْلَا تُسَبِّحُونَ
68:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"

68:29 قَالُوا۟ سُبْحَـٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَـٰلِمِينَ
68:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."

68:30 فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَلَـٰوَمُونَ
68:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.

68:31 قَالُوا۟ يَـٰوَيْلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَـٰغِينَ
68:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."

68:32 عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبْدِلَنَا خَيْرًا مِّنْهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ
68:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."

68:33 كَذَٰلِكَ ٱلْعَذَابُ ۖ وَلَعَذَابُ ٱلْـَٔاخِرَةِ أَكْبَرُ ۚ لَوْ كَانُوا۟ يَعْلَمُونَ
68:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.

68:34 إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ
68:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.

68:35 أَفَنَجْعَلُ ٱلْمُسْلِمِينَ كَٱلْمُجْرِمِينَ
68:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?

68:36 مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ
68:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?

68:37 أَمْ لَكُمْ كِتَـٰبٌ فِيهِ تَدْرُسُونَ
68:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?

68:38 إِنَّ لَكُمْ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ
68:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?

68:39 أَمْ لَكُمْ أَيْمَـٰنٌ عَلَيْنَا بَـٰلِغَةٌ إِلَىٰ يَوْمِ ٱلْقِيَـٰمَةِ ۙ إِنَّ لَكُمْ لَمَا تَحْكُمُونَ
68:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?

68:40 سَلْهُمْ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ
68:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?

68:41 أَمْ لَهُمْ شُرَكَآءُ فَلْيَأْتُوا۟ بِشُرَكَآئِهِمْ إِن كَانُوا۟ صَـٰدِقِينَ
68:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.

68:42 يَوْمَ يُكْشَفُ عَن سَاقٍ وَيُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ فَلَا يَسْتَطِيعُونَ
68:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.

68:43 خَـٰشِعَةً أَبْصَـٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۖ وَقَدْ كَانُوا۟ يُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ وَهُمْ سَـٰلِمُونَ
68:43
Abubakar Gumi (Hausa) :
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).

68:44 فَذَرْنِى وَمَن يُكَذِّبُ بِهَـٰذَا ٱلْحَدِيثِ ۖ سَنَسْتَدْرِجُهُم مِّنْ حَيْثُ لَا يَعْلَمُونَ
68:44
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.

68:45 وَأُمْلِى لَهُمْ ۚ إِنَّ كَيْدِى مَتِينٌ
68:45
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.

68:46 أَمْ تَسْـَٔلُهُمْ أَجْرًا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍ مُّثْقَلُونَ
68:46
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?

68:47 أَمْ عِندَهُمُ ٱلْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ
68:47
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?

68:48 فَٱصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلْحُوتِ إِذْ نَادَىٰ وَهُوَ مَكْظُومٌ
68:48
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.

68:49 لَّوْلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعْمَةٌ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلْعَرَآءِ وَهُوَ مَذْمُومٌ
68:49
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.

68:50 فَٱجْتَبَـٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ
68:50
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.

68:51 وَإِن يَكَادُ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لَيُزْلِقُونَكَ بِأَبْصَـٰرِهِمْ لَمَّا سَمِعُوا۟ ٱلذِّكْرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُۥ لَمَجْنُونٌ
68:51
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"

68:52 وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَـٰلَمِينَ
68:52
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.