Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

82 Al-'Infiţār ٱلْإِنْفِطَار

< Previous   19 Āyah   The Cleaving      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

82:1 إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنفَطَرَتْ
82:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Idan sama ta tsãge.

82:2 وَإِذَا ٱلْكَوَاكِبُ ٱنتَثَرَتْ
82:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan taurãri suka wãtse.

82:3 وَإِذَا ٱلْبِحَارُ فُجِّرَتْ
82:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan tẽkuna aka facce su.

82:4 وَإِذَا ٱلْقُبُورُ بُعْثِرَتْ
82:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan kaburbura aka tõne su.

82:5 عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا قَدَّمَتْ وَأَخَّرَتْ
82:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.

82:6 يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ ٱلْكَرِيمِ
82:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.

82:7 ٱلَّذِى خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ
82:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.

82:8 فِىٓ أَىِّ صُورَةٍ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ
82:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.

82:9 كَلَّا بَلْ تُكَذِّبُونَ بِٱلدِّينِ
82:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!

82:10 وَإِنَّ عَلَيْكُمْ لَحَـٰفِظِينَ
82:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.

82:11 كِرَامًا كَـٰتِبِينَ
82:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mãsu daraja, marubũta.

82:12 يَعْلَمُونَ مَا تَفْعَلُونَ
82:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.

82:13 إِنَّ ٱلْأَبْرَارَ لَفِى نَعِيمٍ
82:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.

82:14 وَإِنَّ ٱلْفُجَّارَ لَفِى جَحِيمٍ
82:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.

82:15 يَصْلَوْنَهَا يَوْمَ ٱلدِّينِ
82:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.

82:16 وَمَا هُمْ عَنْهَا بِغَآئِبِينَ
82:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã zã su faku daga gare ta ba.

82:17 وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلدِّينِ
82:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako?

82:18 ثُمَّ مَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلدِّينِ
82:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?

82:19 يَوْمَ لَا تَمْلِكُ نَفْسٌ لِّنَفْسٍ شَيْـًٔا ۖ وَٱلْأَمْرُ يَوْمَئِذٍ لِّلَّهِ
82:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake.