Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

77 Al-Mursalāt ٱلْمُرْسَلَات

< Previous   50 Āyah   The Emissaries      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

77:1 وَٱلْمُرْسَلَـٰتِ عُرْفًا
77:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ina rantsuwa da iskõkin da ake sakõwa jẽre, sunã bin jũna.

77:2 فَٱلْعَـٰصِفَـٰتِ عَصْفًا
77:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, su zamã iskõki mãsu ƙarfi suna kaɗãwa da ƙarfi.

77:3 وَٱلنَّـٰشِرَٰتِ نَشْرًا
77:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, mãsu watsa rahama wãtsãwa.

77:4 فَٱلْفَـٰرِقَـٰتِ فَرْقًا
77:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
sa'an nan, da ãyõyi mãsu rarrabe gaskiya da ƙarya rarrabẽwa.

77:5 فَٱلْمُلْقِيَـٰتِ ذِكْرًا
77:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan da malã'iku mãsu jẽfa tunãtarwa ga Manzanni.

77:6 عُذْرًا أَوْ نُذْرًا
77:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Domin yanke hamzari ko dõmin gargadi.

77:7 إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَوَٰقِعٌ
77:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, abin da ake yi muku wa'adi da shi tabbas mai aukuwa ne

77:8 فَإِذَا ٱلنُّجُومُ طُمِسَتْ
77:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, idan taurãri aka shãfe haskensu.

77:9 وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ فُرِجَتْ
77:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, idan sama aka tsãge ta.

77:10 وَإِذَا ٱلْجِبَالُ نُسِفَتْ
77:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, idan duwãtsu aka nike su.

77:11 وَإِذَا ٱلرُّسُلُ أُقِّتَتْ
77:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, idan manzanni aka ƙayyade lõkacin tãra su.

77:12 لِأَىِّ يَوْمٍ أُجِّلَتْ
77:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Domin babbar rãnar da aka yi wa ajali.

77:13 لِيَوْمِ ٱلْفَصْلِ
77:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Domin rãnar rarrabẽwa.

77:14 وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ
77:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, me ya sanar da kai rãnar rarrabẽwa?

77:15 وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
77:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone yã tabbata a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

77:16 أَلَمْ نُهْلِكِ ٱلْأَوَّلِينَ
77:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe, ba Mu halakar da (mãsu ƙaryatãw) na farko ba.

77:17 ثُمَّ نُتْبِعُهُمُ ٱلْـَٔاخِرِينَ
77:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, kuma zã Mu biyar musu da na ƙarshe?

77:18 كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِٱلْمُجْرِمِينَ
77:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Haka nan, Muke aikatãwa da mãsu yin laifi.

77:19 وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
77:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa!

77:20 أَلَمْ نَخْلُقكُّم مِّن مَّآءٍ مَّهِينٍ
77:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe, ba Mu halitta ku daga wani ruwa wulakantacce ba.

77:21 فَجَعَلْنَـٰهُ فِى قَرَارٍ مَّكِينٍ
77:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan Muka sanya shi a cikin wani wurin natsuwa amintacce.

77:22 إِلَىٰ قَدَرٍ مَّعْلُومٍ
77:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Zuwa ga wani gwargwadon mudda sananna.

77:23 فَقَدَرْنَا فَنِعْمَ ٱلْقَـٰدِرُونَ
77:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, Muka nũna iyãwarMu? Madalla da Mu, Mãsu nũna iyãwa.

77:24 وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
77:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone ya tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa!

77:25 أَلَمْ نَجْعَلِ ٱلْأَرْضَ كِفَاتًا
77:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe, ba Mu sanya ƙasa matattarã ba.

77:26 أَحْيَآءً وَأَمْوَٰتًا
77:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ga rãyayyu da matattu,

77:27 وَجَعَلْنَا فِيهَا رَوَٰسِىَ شَـٰمِخَـٰتٍ وَأَسْقَيْنَـٰكُم مَّآءً فُرَاتًا
77:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, Muka sanya, a cikinta, kafaffun duwãtsu maɗaukaka, kuma Muka shayar da ku ruwa mai dãɗi?

77:28 وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
77:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

77:29 ٱنطَلِقُوٓا۟ إِلَىٰ مَا كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ
77:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ku tafi zuwa ga abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi!

77:30 ٱنطَلِقُوٓا۟ إِلَىٰ ظِلٍّ ذِى ثَلَـٰثِ شُعَبٍ
77:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ku tafi zuwa ga wata inuwa mai rassa uku.

77:31 لَّا ظَلِيلٍ وَلَا يُغْنِى مِنَ ٱللَّهَبِ
77:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ita ba inuwar ba, kuma ba ta wadãtarwa daga harshen wuta.

77:32 إِنَّهَا تَرْمِى بِشَرَرٍ كَٱلْقَصْرِ
77:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, ita, tanã jifã da tartsatsi kamar sõraye.

77:33 كَأَنَّهُۥ جِمَـٰلَتٌ صُفْرٌ
77:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar dai su raƙumma ne baƙãƙe.

77:34 وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
77:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

77:35 هَـٰذَا يَوْمُ لَا يَنطِقُونَ
77:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wannan, yini ne da bã zã su iya yin magana ba.

77:36 وَلَا يُؤْذَنُ لَهُمْ فَيَعْتَذِرُونَ
77:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã zã a yi musu izni ba, balle su kãwo hanzari.

77:37 وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
77:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

77:38 هَـٰذَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ ۖ جَمَعْنَـٰكُمْ وَٱلْأَوَّلِينَ
77:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wannan rãnar rarrabẽwa ce, Mun tattara ku tare da mutãnen farko.

77:39 فَإِن كَانَ لَكُمْ كَيْدٌ فَكِيدُونِ
77:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, idan akwai wata dabara gare ku, sai ku yi ma Ni ita.

77:40 وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
77:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

77:41 إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى ظِلَـٰلٍ وَعُيُونٍ
77:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, mãsu taƙawa suna a cikin inuwõwi da marẽmari.

77:42 وَفَوَٰكِهَ مِمَّا يَشْتَهُونَ
77:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wasu 'ya'yan itãce irin waɗanda suke marmari.

77:43 كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ
77:43
Abubakar Gumi (Hausa) :
(A ce musu) "Ku ci ku sha cikin ni'ima sabõda abin da kuka kasance kuna aikatãwa."

77:44 إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ
77:44
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, Mũ haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

77:45 وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
77:45
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

77:46 كُلُوا۟ وَتَمَتَّعُوا۟ قَلِيلًا إِنَّكُم مُّجْرِمُونَ
77:46
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Ana ce musu) "Ku ci ku ji ɗan dãdi kaɗan, lalle ne dai ku mãsu laifi ne."

77:47 وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
77:47
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

77:48 وَإِذَا قِيلَ لَهُمُ ٱرْكَعُوا۟ لَا يَرْكَعُونَ
77:48
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, idan an ce musu: "Ku yi rukũ'i; bã zã su yi rukũ'in (salla) ba."

77:49 وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
77:49
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

77:50 فَبِأَىِّ حَدِيثٍۭ بَعْدَهُۥ يُؤْمِنُونَ
77:50
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, da wane lãbãri (Littãfi), waninsa (Alƙur'ãni) zã su yi ĩmãni