Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

78 An-Naba' ٱلنَّبَأ

< Previous   40 Āyah   The Tidings      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

78:1 عَمَّ يَتَسَآءَلُونَ
78:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
A kan mẽ suke tambayar jũna?

78:2 عَنِ ٱلنَّبَإِ ٱلْعَظِيمِ
78:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur'ãni)?

78:3 ٱلَّذِى هُمْ فِيهِ مُخْتَلِفُونَ
78:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?

78:4 كَلَّا سَيَعْلَمُونَ
78:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Zã su sani.

78:5 ثُمَّ كَلَّا سَيَعْلَمُونَ
78:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, a'aha! Zã su sani.

78:6 أَلَمْ نَجْعَلِ ٱلْأَرْضَ مِهَـٰدًا
78:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?

78:7 وَٱلْجِبَالَ أَوْتَادًا
78:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?

78:8 وَخَلَقْنَـٰكُمْ أَزْوَٰجًا
78:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?

78:9 وَجَعَلْنَا نَوْمَكُمْ سُبَاتًا
78:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?

78:10 وَجَعَلْنَا ٱلَّيْلَ لِبَاسًا
78:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?

78:11 وَجَعَلْنَا ٱلنَّهَارَ مَعَاشًا
78:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?

78:12 وَبَنَيْنَا فَوْقَكُمْ سَبْعًا شِدَادًا
78:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?

78:13 وَجَعَلْنَا سِرَاجًا وَهَّاجًا
78:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?

78:14 وَأَنزَلْنَا مِنَ ٱلْمُعْصِرَٰتِ مَآءً ثَجَّاجًا
78:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?

78:15 لِّنُخْرِجَ بِهِۦ حَبًّا وَنَبَاتًا
78:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?

78:16 وَجَنَّـٰتٍ أَلْفَافًا
78:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?

78:17 إِنَّ يَوْمَ ٱلْفَصْلِ كَانَ مِيقَـٰتًا
78:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.

78:18 يَوْمَ يُنفَخُ فِى ٱلصُّورِ فَتَأْتُونَ أَفْوَاجًا
78:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.

78:19 وَفُتِحَتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ أَبْوَٰبًا
78:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.

78:20 وَسُيِّرَتِ ٱلْجِبَالُ فَكَانَتْ سَرَابًا
78:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.

78:21 إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتْ مِرْصَادًا
78:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.

78:22 لِّلطَّـٰغِينَ مَـَٔابًا
78:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.

78:23 لَّـٰبِثِينَ فِيهَآ أَحْقَابًا
78:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.

78:24 لَّا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرْدًا وَلَا شَرَابًا
78:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.

78:25 إِلَّا حَمِيمًا وَغَسَّاقًا
78:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.

78:26 جَزَآءً وِفَاقًا
78:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sakamako mai dãcẽwa.

78:27 إِنَّهُمْ كَانُوا۟ لَا يَرْجُونَ حِسَابًا
78:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.

78:28 وَكَذَّبُوا۟ بِـَٔايَـٰتِنَا كِذَّابًا
78:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyinMu, ƙaryatãwa!

78:29 وَكُلَّ شَىْءٍ أَحْصَيْنَـٰهُ كِتَـٰبًا
78:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.

78:30 فَذُوقُوا۟ فَلَن نَّزِيدَكُمْ إِلَّا عَذَابًا
78:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.

78:31 إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ مَفَازًا
78:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.

78:32 حَدَآئِقَ وَأَعْنَـٰبًا
78:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lambuna da inabõbi.

78:33 وَكَوَاعِبَ أَتْرَابًا
78:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da cikakkun 'yammata, tsãrar jũna.

78:34 وَكَأْسًا دِهَاقًا
78:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da hinjãlan giya cikakku.

78:35 لَّا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًا وَلَا كِذَّٰبًا
78:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.

78:36 جَزَآءً مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابًا
78:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.

78:37 رَّبِّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ٱلرَّحْمَـٰنِ ۖ لَا يَمْلِكُونَ مِنْهُ خِطَابًا
78:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.

78:38 يَوْمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ صَفًّا ۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنْ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحْمَـٰنُ وَقَالَ صَوَابًا
78:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.

78:39 ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلْحَقُّ ۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ مَـَٔابًا
78:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.

78:40 إِنَّآ أَنذَرْنَـٰكُمْ عَذَابًا قَرِيبًا يَوْمَ يَنظُرُ ٱلْمَرْءُ مَا قَدَّمَتْ يَدَاهُ وَيَقُولُ ٱلْكَافِرُ يَـٰلَيْتَنِى كُنتُ تُرَٰبًۢا
78:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"