Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

80 `Abasa عَبَسَ

< Previous   42 Āyah   He Frowned      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

80:1 عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ
80:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yã game huska kuma ya jũya bãya.

80:2 أَن جَآءَهُ ٱلْأَعْمَىٰ
80:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda makãho yã je masa.

80:3 وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ
80:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

80:4 أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكْرَىٰٓ
80:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

80:5 أَمَّا مَنِ ٱسْتَغْنَىٰ
80:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

80:6 فَأَنتَ لَهُۥ تَصَدَّىٰ
80:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

80:7 وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ
80:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

80:8 وَأَمَّا مَن جَآءَكَ يَسْعَىٰ
80:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

80:9 وَهُوَ يَخْشَىٰ
80:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

80:10 فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ
80:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kai kuma kã shagala ga barinsa!

80:11 كَلَّآ إِنَّهَا تَذْكِرَةٌ
80:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

80:12 فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ
80:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

80:13 فِى صُحُفٍ مُّكَرَّمَةٍ
80:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

80:14 مَّرْفُوعَةٍ مُّطَهَّرَةٍۭ
80:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

80:15 بِأَيْدِى سَفَرَةٍ
80:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

80:16 كِرَامٍۭ بَرَرَةٍ
80:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

80:17 قُتِلَ ٱلْإِنسَـٰنُ مَآ أَكْفَرَهُۥ
80:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

80:18 مِنْ أَىِّ شَىْءٍ خَلَقَهُۥ
80:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

80:19 مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ
80:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

80:20 ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ
80:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

80:21 ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقْبَرَهُۥ
80:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

80:22 ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ
80:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

80:23 كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَآ أَمَرَهُۥ
80:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

80:24 فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَـٰنُ إِلَىٰ طَعَامِهِۦٓ
80:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

80:25 أَنَّا صَبَبْنَا ٱلْمَآءَ صَبًّا
80:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

80:26 ثُمَّ شَقَقْنَا ٱلْأَرْضَ شَقًّا
80:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

80:27 فَأَنۢبَتْنَا فِيهَا حَبًّا
80:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

80:28 وَعِنَبًا وَقَضْبًا
80:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da inabi da ciyãwa.

80:29 وَزَيْتُونًا وَنَخْلًا
80:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da zaitũni da itãcen dabĩno.

80:30 وَحَدَآئِقَ غُلْبًا
80:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da lambuna, mãsu yawan itãce.

80:31 وَفَـٰكِهَةً وَأَبًّا
80:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

80:32 مَّتَـٰعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ
80:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

80:33 فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ
80:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

80:34 يَوْمَ يَفِرُّ ٱلْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ
80:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

80:35 وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ
80:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da uwarsa da ubansa.

80:36 وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ
80:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da mãtarsa da ɗiyansa.

80:37 لِكُلِّ ٱمْرِئٍ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍ شَأْنٌ يُغْنِيهِ
80:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

80:38 وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ مُّسْفِرَةٌ
80:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

80:39 ضَاحِكَةٌ مُّسْتَبْشِرَةٌ
80:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

80:40 وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌ
80:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

80:41 تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ
80:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
Baƙi zai rufe su.

80:42 أُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْكَفَرَةُ ٱلْفَجَرَةُ
80:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).