Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

56 Al-Wāqi`ah ٱلْوَاقِعَة

< Previous   96 Āyah   The Inevitable      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

56:1 إِذَا وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ
56:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Idan mai aukuwa ta auku.

56:2 لَيْسَ لِوَقْعَتِهَا كَاذِبَةٌ
56:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.

56:3 خَافِضَةٌ رَّافِعَةٌ
56:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.

56:4 إِذَا رُجَّتِ ٱلْأَرْضُ رَجًّا
56:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.

56:5 وَبُسَّتِ ٱلْجِبَالُ بَسًّا
56:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.

56:6 فَكَانَتْ هَبَآءً مُّنۢبَثًّا
56:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.

56:7 وَكُنتُمْ أَزْوَٰجًا ثَلَـٰثَةً
56:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma kun kasance nau'i uku.

56:8 فَأَصْحَـٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ مَآ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ
56:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Watau mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?

56:9 وَأَصْحَـٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ مَآ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ
56:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?

56:10 وَٱلسَّـٰبِقُونَ ٱلسَّـٰبِقُونَ
56:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,

56:11 أُو۟لَـٰٓئِكَ ٱلْمُقَرَّبُونَ
56:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.

56:12 فِى جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ
56:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
A ckin Aljannar ni'ima.

56:13 ثُلَّةٌ مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ
56:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Jama'a ne daga mutãnen farko.

56:14 وَقَلِيلٌ مِّنَ ٱلْـَٔاخِرِينَ
56:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.

56:15 عَلَىٰ سُرُرٍ مَّوْضُونَةٍ
56:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.

56:16 مُّتَّكِـِٔينَ عَلَيْهَا مُتَقَـٰبِلِينَ
56:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.

56:17 يَطُوفُ عَلَيْهِمْ وِلْدَٰنٌ مُّخَلَّدُونَ
56:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.

56:18 بِأَكْوَابٍ وَأَبَارِيقَ وَكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍ
56:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.

56:19 لَّا يُصَدَّعُونَ عَنْهَا وَلَا يُنزِفُونَ
56:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.

56:20 وَفَـٰكِهَةٍ مِّمَّا يَتَخَيَّرُونَ
56:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.

56:21 وَلَحْمِ طَيْرٍ مِّمَّا يَشْتَهُونَ
56:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.

56:22 وَحُورٌ عِينٌ
56:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.

56:23 كَأَمْثَـٰلِ ٱللُّؤْلُؤِ ٱلْمَكْنُونِ
56:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.

56:24 جَزَآءًۢ بِمَا كَانُوا۟ يَعْمَلُونَ
56:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.

56:25 لَا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًا وَلَا تَأْثِيمًا
56:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.

56:26 إِلَّا قِيلًا سَلَـٰمًا سَلَـٰمًا
56:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.

56:27 وَأَصْحَـٰبُ ٱلْيَمِينِ مَآ أَصْحَـٰبُ ٱلْيَمِينِ
56:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?

56:28 فِى سِدْرٍ مَّخْضُودٍ
56:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.

56:29 وَطَلْحٍ مَّنضُودٍ
56:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.

56:30 وَظِلٍّ مَّمْدُودٍ
56:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.

56:31 وَمَآءٍ مَّسْكُوبٍ
56:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wani ruwa mai gudãna.

56:32 وَفَـٰكِهَةٍ كَثِيرَةٍ
56:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.

56:33 لَّا مَقْطُوعَةٍ وَلَا مَمْنُوعَةٍ
56:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã su yankẽwa kuma bã a hana su.

56:34 وَفُرُشٍ مَّرْفُوعَةٍ
56:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.

56:35 إِنَّآ أَنشَأْنَـٰهُنَّ إِنشَآءً
56:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.

56:36 فَجَعَلْنَـٰهُنَّ أَبْكَارًا
56:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan Muka sanya su budurwai.

56:37 عُرُبًا أَتْرَابًا
56:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.

56:38 لِّأَصْحَـٰبِ ٱلْيَمِينِ
56:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ga mazõwa dãma.

56:39 ثُلَّةٌ مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ
56:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.

56:40 وَثُلَّةٌ مِّنَ ٱلْـَٔاخِرِينَ
56:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.

56:41 وَأَصْحَـٰبُ ٱلشِّمَالِ مَآ أَصْحَـٰبُ ٱلشِّمَالِ
56:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?

56:42 فِى سَمُومٍ وَحَمِيمٍ
56:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.

56:43 وَظِلٍّ مِّن يَحْمُومٍ
56:43
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.

56:44 لَّا بَارِدٍ وَلَا كَرِيمٍ
56:44
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.

56:45 إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَبْلَ ذَٰلِكَ مُتْرَفِينَ
56:45
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.

56:46 وَكَانُوا۟ يُصِرُّونَ عَلَى ٱلْحِنثِ ٱلْعَظِيمِ
56:46
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.

56:47 وَكَانُوا۟ يَقُولُونَ أَئِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَـٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ
56:47
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"

56:48 أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ
56:48
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"

56:49 قُلْ إِنَّ ٱلْأَوَّلِينَ وَٱلْـَٔاخِرِينَ
56:49
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."

56:50 لَمَجْمُوعُونَ إِلَىٰ مِيقَـٰتِ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ
56:50
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."

56:51 ثُمَّ إِنَّكُمْ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلْمُكَذِّبُونَ
56:51
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"

56:52 لَـَٔاكِلُونَ مِن شَجَرٍ مِّن زَقُّومٍ
56:52
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."

56:53 فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ
56:53
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."

56:54 فَشَـٰرِبُونَ عَلَيْهِ مِنَ ٱلْحَمِيمِ
56:54
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."

56:55 فَشَـٰرِبُونَ شُرْبَ ٱلْهِيمِ
56:55
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."

56:56 هَـٰذَا نُزُلُهُمْ يَوْمَ ٱلدِّينِ
56:56
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.

56:57 نَحْنُ خَلَقْنَـٰكُمْ فَلَوْلَا تُصَدِّقُونَ
56:57
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?

56:58 أَفَرَءَيْتُم مَّا تُمْنُونَ
56:58
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?

56:59 ءَأَنتُمْ تَخْلُقُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلْخَـٰلِقُونَ
56:59
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?

56:60 نَحْنُ قَدَّرْنَا بَيْنَكُمُ ٱلْمَوْتَ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ
56:60
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba,

56:61 عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ أَمْثَـٰلَكُمْ وَنُنشِئَكُمْ فِى مَا لَا تَعْلَمُونَ
56:61
Abubakar Gumi (Hausa) :
A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.

56:62 وَلَقَدْ عَلِمْتُمُ ٱلنَّشْأَةَ ٱلْأُولَىٰ فَلَوْلَا تَذَكَّرُونَ
56:62
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?

56:63 أَفَرَءَيْتُم مَّا تَحْرُثُونَ
56:63
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?

56:64 ءَأَنتُمْ تَزْرَعُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلزَّٰرِعُونَ
56:64
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?

56:65 لَوْ نَشَآءُ لَجَعَلْنَـٰهُ حُطَـٰمًا فَظَلْتُمْ تَفَكَّهُونَ
56:65
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.

56:66 إِنَّا لَمُغْرَمُونَ
56:66
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"

56:67 بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ
56:67
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"

56:68 أَفَرَءَيْتُمُ ٱلْمَآءَ ٱلَّذِى تَشْرَبُونَ
56:68
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?

56:69 ءَأَنتُمْ أَنزَلْتُمُوهُ مِنَ ٱلْمُزْنِ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنزِلُونَ
56:69
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?

56:70 لَوْ نَشَآءُ جَعَلْنَـٰهُ أُجَاجًا فَلَوْلَا تَشْكُرُونَ
56:70
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?

56:71 أَفَرَءَيْتُمُ ٱلنَّارَ ٱلَّتِى تُورُونَ
56:71
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?

56:72 ءَأَنتُمْ أَنشَأْتُمْ شَجَرَتَهَآ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنشِـُٔونَ
56:72
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?

56:73 نَحْنُ جَعَلْنَـٰهَا تَذْكِرَةً وَمَتَـٰعًا لِّلْمُقْوِينَ
56:73
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.

56:74 فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ
56:74
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.

56:75 ۞ فَلَآ أُقْسِمُ بِمَوَٰقِعِ ٱلنُّجُومِ
56:75
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.

56:76 وَإِنَّهُۥ لَقَسَمٌ لَّوْ تَعْلَمُونَ عَظِيمٌ
56:76
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.

56:77 إِنَّهُۥ لَقُرْءَانٌ كَرِيمٌ
56:77
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.

56:78 فِى كِتَـٰبٍ مَّكْنُونٍ
56:78
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikin wani littafi tsararre.

56:79 لَّا يَمَسُّهُۥٓ إِلَّا ٱلْمُطَهَّرُونَ
56:79
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.

56:80 تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
56:80
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.

56:81 أَفَبِهَـٰذَا ٱلْحَدِيثِ أَنتُم مُّدْهِنُونَ
56:81
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?

56:82 وَتَجْعَلُونَ رِزْقَكُمْ أَنَّكُمْ تُكَذِّبُونَ
56:82
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?

56:83 فَلَوْلَآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلْحُلْقُومَ
56:83
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).

56:84 وَأَنتُمْ حِينَئِذٍ تَنظُرُونَ
56:84
Abubakar Gumi (Hausa) :
Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.

56:85 وَنَحْنُ أَقْرَبُ إِلَيْهِ مِنكُمْ وَلَـٰكِن لَّا تُبْصِرُونَ
56:85
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.

56:86 فَلَوْلَآ إِن كُنتُمْ غَيْرَ مَدِينِينَ
56:86
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?

56:87 تَرْجِعُونَهَآ إِن كُنتُمْ صَـٰدِقِينَ
56:87
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.

56:88 فَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُقَرَّبِينَ
56:88
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,

56:89 فَرَوْحٌ وَرَيْحَانٌ وَجَنَّتُ نَعِيمٍ
56:89
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.

56:90 وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنْ أَصْحَـٰبِ ٱلْيَمِينِ
56:90
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,

56:91 فَسَلَـٰمٌ لَّكَ مِنْ أَصْحَـٰبِ ٱلْيَمِينِ
56:91
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.

56:92 وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُكَذِّبِينَ ٱلضَّآلِّينَ
56:92
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,

56:93 فَنُزُلٌ مِّنْ حَمِيمٍ
56:93
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.

56:94 وَتَصْلِيَةُ جَحِيمٍ
56:94
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da ƙõnuwa da Jahĩm,

56:95 إِنَّ هَـٰذَا لَهُوَ حَقُّ ٱلْيَقِينِ
56:95
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.

56:96 فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ
56:96
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.