Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

89 Al-Fajr ٱلْفَجْر

< Previous   30 Āyah   The Dawn      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

89:1 وَٱلْفَجْرِ
89:1 Inã rantsuwa da alfijiri. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:2 وَلَيَالٍ عَشْرٍ
89:2 Da darũruwa gõma. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:3 وَٱلشَّفْعِ وَٱلْوَتْرِ
89:3 Da (adadi na) cikã da (na) mãrã. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:4 وَٱلَّيْلِ إِذَا يَسْرِ
89:4 Da dare idan yana shũɗewa. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:5 هَلْ فِى ذَٰلِكَ قَسَمٌ لِّذِى حِجْرٍ
89:5 Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)? - Abubakar Gumi (Hausa)

89:6 أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ
89:6 Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba? - Abubakar Gumi (Hausa)

89:7 إِرَمَ ذَاتِ ٱلْعِمَادِ
89:7 Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:8 ٱلَّتِى لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِى ٱلْبِلَـٰدِ
89:8 Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya). - Abubakar Gumi (Hausa)

89:9 وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُوا۟ ٱلصَّخْرَ بِٱلْوَادِ
89:9 Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)? - Abubakar Gumi (Hausa)

89:10 وَفِرْعَوْنَ ذِى ٱلْأَوْتَادِ
89:10 Da Fir'auna mai turãku. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:11 ٱلَّذِينَ طَغَوْا۟ فِى ٱلْبِلَـٰدِ
89:11 Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa? - Abubakar Gumi (Hausa)

89:12 فَأَكْثَرُوا۟ فِيهَا ٱلْفَسَادَ
89:12 Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:13 فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ
89:13 Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:14 إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلْمِرْصَادِ
89:14 Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:15 فَأَمَّا ٱلْإِنسَـٰنُ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكْرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَكْرَمَنِ
89:15 To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni." - Abubakar Gumi (Hausa)

89:16 وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَهَـٰنَنِ
89:16 Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni." - Abubakar Gumi (Hausa)

89:17 كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ ٱلْيَتِيمَ
89:17 A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya! - Abubakar Gumi (Hausa)

89:18 وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ
89:18 Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci! - Abubakar Gumi (Hausa)

89:19 وَتَأْكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكْلًا لَّمًّا
89:19 Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:20 وَتُحِبُّونَ ٱلْمَالَ حُبًّا جَمًّا
89:20 Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:21 كَلَّآ إِذَا دُكَّتِ ٱلْأَرْضُ دَكًّا دَكًّا
89:21 A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:22 وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلْمَلَكُ صَفًّا صَفًّا
89:22 Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:23 وَجِا۟ىٓءَ يَوْمَئِذٍۭ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكْرَىٰ
89:23 Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi! - Abubakar Gumi (Hausa)

89:24 يَقُولُ يَـٰلَيْتَنِى قَدَّمْتُ لِحَيَاتِى
89:24 Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!" - Abubakar Gumi (Hausa)

89:25 فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٌ
89:25 To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:26 وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٌ
89:26 Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa. - Abubakar Gumi (Hausa)

89:27 يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفْسُ ٱلْمُطْمَئِنَّةُ
89:27 Yã kai rai mai natsuwa! - Abubakar Gumi (Hausa)

89:28 ٱرْجِعِىٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةً مَّرْضِيَّةً
89:28 Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira). - Abubakar Gumi (Hausa)

89:29 فَٱدْخُلِى فِى عِبَـٰدِى
89:29 Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya). - Abubakar Gumi (Hausa)

89:30 وَٱدْخُلِى جَنَّتِى
89:30 Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira). - Abubakar Gumi (Hausa)